Tambayoyin Auratayya: 01

แชร์
ฝัง
  • เผยแพร่เมื่อ 16 ต.ค. 2024
  • Wannan Sabon Shiri ne da Babban Malaminmu @amdaurawa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa (Hafizahullah) Ya fara gabatarwa a Ranar 6-Rabi'ul Awwal wanda yayi dai-dai da 02/October/2022. Inda Malamin namu yake amsa tambayoyin da suka shafi auratayya kadai. Ga masu son aiko da nasu tambayoyin sai su tura su zuwa ga akwatun Sakonmu Kamar Haka auratayya101@gmail.com.
    Ga Tambayoyin Kamar Haka:
    1.Assalamualaikum malam fatan mun tashi lfy, Allah ya sa hakan
    Ameen.
    Malam mijina ne yake da matsala, idan ya kusance ni ko yazo inda
    nake gaba daya sai yayi ta korafi nan na ciwo can naciwo ko Kuma
    cikin dare ya tashi yana ta ihu da firgici, malam a haka har ta kai ga
    abun inya tashi yayi ta fada yace shi bazai iya ba ya sakeni, a haka
    yanzu anyi saki uku, yanzu ya dawo wai yaje an mishi fatawa cewa ba
    a cikin hankalinsa yayi ba aure na nan. Malam wannan fatawa da aka
    bashi Tana da inganci ko Bata da asali ?
    2. Aslm Allah ya qara wa malam lfy da nisan kwana malam shin
    yamastayin Wanda yayi Wasa da mace ana azume har azuminsa
    yakarye daga bayan azuminsa yakarye yasadu da matar malam Allah
    ya qara fasaha
    3. Assalamu alaikum akaramakallah ni ina cikin damuwa sosai akwai
    wata yarinya da nake so zan aura mun dade muna soyayya to kuma
    lokaci guda sai na fara fuskantar wasu abubuwan daga gareta karshe
    ma dai yanzu ban kiranta bata kira na na kasa cireta a raina kullum
    tunata nakeyi shine nake so a banj shawara yaza,I na manta da ita a
    rayuwa ta.?
    4.Assalamu alaikum akaramakallah ni ina cikin damuwa sosai akwai
    wata yarinya da nake so zan aura mun dade muna soyayya to kuma
    lokaci guda sai na fara fuskantar wasu abubuwan daga gareta karshe
    ma dai yanzu ban kiranta bata kira na na kasa cireta a raina kullum
    tunata nakeyi shine nake so a banj shawara yaza,I na manta da ita a
    rayuwa ta
    4. Malam muna maka fatan alkhairy Allah ya kara lafiya da nisan
    kwana. Malam shekararmu uku kenan da aure amma mijina baya kula
    da wasu daga cikin hakkokina, yana bani ci da sha da sutura amma
    daga wannan to bani da maraba da roommate a wajensa. Ina mishi
    duk wani abu da nasan ze dawo da hankalinshi wurina amma
    ni kadai ke kidi na nake rawa ta. Nayi mashi magana ba
    sau daya ba ba biyu ba akan hakan yana sa inji yana fita a raina amma
    baya saurarana malam har sai da takai gaba daya naji bana sonshi
    kuma baya burgeni duk abunda yayi har nakan fada masa maganganu
    marasa dadi wani lokacin. Da ya fahimci haka yanzu malam sai yake
    kokarin gyarawa amma wlh ko kadan hakan baya burgeni kuma
    banajin shi a raina saboda hakan. Shin malam akwai laifi in na nemi
    ya sallameni? Saboda Ina gudun na cigaba da Saba mashi Ina Saba
    ma ubangiji na. Malam ku bani shawara. Nagode
    5. Assalamu Alaikum
    Malam Barka da warhaka,Yaya kokari,Allah Ya azurtaku da
    Ikhlaasi, Allah Yasa Aljannah ce Makoma Ameen.
    Malam shin Ya halatta miji ya tilastawa Matarsa Qayyade
    haihuwa (kamar yace yara uku yakeso ta Haifa? sa’annan menene
    hukuncinsa na kaurace mata tsawon wata biyar a dalilin kin
    Amincewarta akan hakan.?

ความคิดเห็น • 20