Ina Da Tsananin Kishi, Ga Miji Na Zaiyi Aure | Tambayoyin Auratayya

แชร์
ฝัง
  • เผยแพร่เมื่อ 23 ธ.ค. 2023
  • Za ku iya turo naku tambayoyin zuwa ga wannan akwatun sakon namu auratayya101@gmail.com
    Ga Tambyaoyin Kamar Haka:
    Tambaya 1
    Assalamu alaikum
    Malam tambaya ta ita ce miji na yana shirin Kara aure sai dai ina da kishi
    Ina kokari wajen kiyaye dokokin Allah bakin gwargwado! mijina da yan uwa
    na da mahaifana da duk wanda zan zauna dashi suna yaba mani wajen
    zamantakewa, Shima mijina yana fadin yasan bazan bashi matsala ba.
    Alhamdulillahi ba alfahari nake ba nasan in sha Allah komai rashin dadin
    zaman da mutum yake dashi ina iya hakuri koda kuwa zan cutu
    Ban taba Kwana da wani a raina ba Kuma komai akayi mani.
    Yanzun dai naji na tsani matar da duk wanda ya santa ina tsoron kada in
    cutar da wani ina tsoron kada halaye na su canza ina tsoron aikata sabo ko
    shirka don Wallahi malam bani son kishiya zan iya neman saki daga mijina
    domin kada in saba ma Allah ina son Aljanna Kuma in samu sauki a zuciyata
    shekarar mu 18 da yara 7 ina aiki Kuma bana tauye mijina ta dalilin aiki na
    Kuma har alfahari yake da haka Nagode daga Asama harissa
    Tambaya 2
    Assslam alaikum
    Malam aurena yakusa kuma a hotel nake zaune zan iya zama da
    matata a hotel kafin agama shirya gidan? Ba a nigeria nake zaune
    ba kuma takusa zuwa matar tawa. Zaman hotel zai albarka kamar
    zaman gida? Ya abun yake malam..?
    ----------------------------------
    Tambaya 3
    Assalamualaikum wa rahamatullahi wa barakatuh. Malam Ina maka
    fatan alkhairi. A Shirin ku na baya naji kun amsa, wata da mijin ta
    yake mu'amalar aure da kishiyarta ko ba kwanan ta bane. Shin
    haramun ne yin hakan? saboda mai gida na ya kan bukace ni ko ba
    ranar kwana na bane. Ko dole sai ya nemi izinin ta?

ความคิดเห็น • 10

  • @user-bn1qh8lw6r
    @user-bn1qh8lw6r 7 หลายเดือนก่อน +1

    Jazakillahu bi khair

  • @user-tv3wl8wb3q
    @user-tv3wl8wb3q 7 หลายเดือนก่อน +1

    Masha Allah Allah yasaka da alkairi

  • @suleynafiou7711
    @suleynafiou7711 7 หลายเดือนก่อน

    ina da mata ama Bata bani kulawa ya da yakamata ku ma tana sona

  • @fuseini.Issifu
    @fuseini.Issifu 7 หลายเดือนก่อน

    MA SHA ALLAH

  • @AbdourazakOumar-jw2zy
    @AbdourazakOumar-jw2zy 7 หลายเดือนก่อน

    Allah qarama malan lafiya wai mace kace tatapi gidansu hakan yana nipinsakine

  • @hanifa3966
    @hanifa3966 7 หลายเดือนก่อน

    Muna masu godiya sosai da irin yadda malam yake tunatar damu,allah yayi albarka da daukaka,Kai kuma Mai dauka allah ya biyaka kaima❤❤❤

  • @HafsatMuhammadidriss-zv4sp
    @HafsatMuhammadidriss-zv4sp 7 หลายเดือนก่อน +1

    جزاکم الله خيرا الجزاء

  • @salissouabdoulrachid4431
    @salissouabdoulrachid4431 7 หลายเดือนก่อน +1

    Assalamou alaikoum warahamatoullah wabarkatouhou Allah ya karama malan lafiya

  • @osmanabassmuhammad4098
    @osmanabassmuhammad4098 7 หลายเดือนก่อน

    جزاكم الله خيرا

  • @AminaAmina-fc2wy
    @AminaAmina-fc2wy 7 หลายเดือนก่อน +1

    Assalamu Alaikum warahamatullahi wabara katuhu malam